Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

EFCC ta kwato kadarori 214 a hannun ‘yan siyasa da jami’an gwamnati

Published

on

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC ta ce tsakanin shekarar 2015 shekarar bara, ta kwato kadarori guda dari biyu da goma sha hudu daga wajen jami’an gwamnati da ‘yan siyasa.

A cewar hukumar ta kwato kadarorin ne a jihohin Lagos da Kaduna da Katsina da Jigawa da Kogi da Adamawa da Oyo da kuma birnin tarayya Abuja.

Cikin kadarorin da hukumar ta sanar, har da rukunin gidaje wadanda aka kwace daga wajen wasu mutane 70 da kuma kamfanoni guda 7.

Bayanan kididdigar kadarorin ta nuna cewa, guda 179 an kwace su ne ta hanyar hukuncin kotu na wucin gadi.

Wasu daga cikin wadanda hukumar ta kwace kadarorin su, sun hada da: tsohon mai bai wa shugaba Goodluck Jonathan shawara kan harkokin yada labarai Ima Niboro da tsohuwar ministar Man fetur Diezani Alison-Madueke da tsohon mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro kanal Sambo Dasuki mai ritaya.

Haka zalika hukumar ta EFCC ta kuma kwace kadarorin tsohon minista Iyorchia Ayu da tsohon babban hafsan tsaro marigayi Air Marshal Alex Badeh da kuma tsohon babban hafsan sojojin sama Air Marshal Adesola Amosu mai ritaya.

Sauran sune: tsohon gwamnan jihar Ekiti Ayodele Fayose da tsohon gwaman jihar Bauchi Isah Yuguda da kanal Bello Fadile mai ritaya da tsofaffin gwamnonin jihohin Niger da Katsina Babangida Aliyu da kuma Ibrahim Shema

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!