Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Katsina:wani jirgin shalkwabta rundanar sojin kasar nan yayi hadari

Published

on

Wani jirgin shalkwabta mallakin rundunar sojojin sama na kasar nan yayi hadari lokacin da ya ke kokarin sauka bayan dawowa daga samame da ya kai ga ‘yan bindiga a jihar Katsina.

Daraktan yada labarai na rundunar sojin sama na kasar nan Air Commodore Ibikunle Daramola ne ya bayyana haka ga manema labarai jiya a Abuja.

A cewar sa jirgion yayi hadari ne da misalin karfe uku da rabi a filin jirgin sama na katsina a jiya Laraba sai dai har ya zuwa yanzu ba akai ga gano musabbabin hatsarin ba.

Air Commodore Ibikunle Daramola ya kuma ce ba a samu hasarar rayuka ba sanadiyar hatsarin.

Haka kuma ya ce babban hafsan sojin sama na kasa Air marshall Sadique Abubakar ya bada umarnin gudanar bincike don gano musabbabin faruwar lamarin.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!