Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Kano: Yan sanda sun kama wani da ake zargin dan Boko Haram

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta bayyana cewa, ta kama wani da ake zargin dan kungiyar Boko Haram ne bayan daya gudo daga garin Maiduguri zuwa nan Kano kuma yake yin basaja a matsayin mahaukaci yana yawon neman sadaka, a unguwar Mandawari dake cikin birnin Kano.

Mutumin wanda har kawo yanzu rundunar ‘yan sandan ba ta bayyana sunan sa ba, rahotonni sun bayyana cewa ya dade yana yawo a unguwannin yankin yana neman sadaka.

A cewar Rundunar ‘yan sandan, wani soja ne da ke aiki a garin na Maiduguri ya dawo gida hutu inda ya ga mtumin a unguwarsu ta Mandawari nan take ya shaida shi inda ya sanar da jami’an ‘yan sanda kuma ana kama shi.

Da yake jawabi ga manema labarai, kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kano, DSP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya bayyana cewa tuni kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano Ahmad Iliyasu ya bada umarnin mika shi shalkwatar rundunar da ke unguwar Bompai domin fadada bincike.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!