Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Fitar Zaki a Kano: Akwai bukatar duba na tsanaki kan gidan adana dabbobin daji

Published

on

Kai tsaye: Har yanzu ba’a kama Zakin da ya kubuce ba

Bayan da rikakken zakin nan da ya kwace a gidan adana dabbobin daji na jihar Kano ya koma kejinsa bayan shafe awanni 40 ana fama da shi, masana da dama dai na bayyana cewa, akwai bukatar mahukunta jihar su yi duba na tsanaki kan gidan ta hanyar lalubo hanyoyin da za su kare aukuwar makamanciyar matsalar a gaba.

Daga cikin abinda masanan ke magana a kai sun hadar da samar da ingantattu kuma wadatattun kayan aikin kula da dabbobin, tare da kara yawan adadin abincin da ake ciyar da dabbobin.

A nazarin na masana dai, sun bayyana cewa, daga cikin matsalolin da gidan ke fuskanta akwai rashin isassun kayan aiki da ya sa har sai da aka nemo allurar da za ta kashe kuzarin zakin daga birnin tarayya Abuja, kasancewar babu ita a nan Kano, inda hakan ya baiwa zakin damar kwashe kusan kwanaki 2 ana fama da shi kafin ya koma kejin nasa.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!