Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Manyan Labarai

Yaran Kano 9: Ganduje ya kafa kwamitin bincike na musamman

Published

on

Gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje ya kafa wani kwamitin bincike, don bin diddigin kan kwato hakkokin yaran nan 9 da aka ceto daga hannun masu satar mutane da suka sayar da su a Jihar Anambra.

Daga cikin aikin da kwmaitin zai yi shi ne, bibiyar duk mutanen da aka sace a nan Kano tun daga shekarar 2010 zuwa yanzu ta hanyar jin ra’ayoyin shaidu ta baka ko a rubuce, domin samun makama a kan binciken, tare da gano dalilan batan na su.

Sakataren yada labaran gwamnan Abba Anwar ne bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar yau Juma’a, inda ya bayyana cewa Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana sunan Justice Wada Umar Rano a matsayin wanda zai jagoranci kwamitin.

Sanarwar ta kara da cewa, ranar alhamis mai zuwa 31 ga watan Oktoban nan da mu ke ciki gwamnan zai kaddamar da kwamaitin.

Tun a cikin shekarar 2015 ne dai al’ummar Unguwannin Hotoro da Kawo da Walalambe da Walawai da kuma Tinshama dukkansu a karamar hukumar Nassarawa a Kano, suka koka da cewa an sace mu su yara akalla 47.

A baya-bayan nan ne dai rundunar yan sandan Jihar Kano ta bankado gungun masu satar yaran suna sayar da su Jihar Anambra tare da sauya mu su addini zuwa kiristoci, inda ta ceto yara 9 daga hannunsu.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!