Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kano 9 Kids: Yara 113 aka sace daga Kano zuwa Kudu – Kwamitin bincike

Published

on

Kwamatin bada shawarwari kan sace-sacen yara ‘yan asalin jihar Kano zuwa wasu daga cikin jihohin kudancin kasar nan ya ce zai fara daukan hanyoyi biyar cikin 46 da ya mikawa gwamnatin jihar a makon daya gabata da zai aiwatar da aikin magance matsalar satar yaran.

Shugaban kwamatin Justice Wada Umar Rano, ne ya bayyan hakan yau yayin da yake zantawa da manema labarai game da hanyoyin da kwamitin zai bi domin fara aiwatar da aikin nasa.

Wada Umar Rano ya ce biyu daga cikin matakai biyar din da kwamatin zai fara aiki a kansa ya hadar da gurfanar da wadanda aka kama da laifin satar yaran a gaban Kotu da kuma tashin tashar mota ta New Road dake sabon gari zuwa wani guri na daban.

Karin labarai:

Yaran Kano 9: Ganduje ya kafa kwamitin bincike na musamman

Kano9: Karanta cikakken labarin yaran Kano da aka sace

Justice Wada Umar Rano ya kara da cewa kwamatin ya gano cewa yaran da ake tunanin an sace ‘yan asalin jihar Kano daga shekarar 2010 zuwa shekarar da muke ciki ta 2019 sun kai su 113.

Ya kuma ce zuwa yanzu an bai wa iyayen yaran da aka sace naira miliyan guda kowannen su, da kuma kula da ilimin yaran tun daga Firamare zuwa Sakandire da kuma jami’a.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!