Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Sarkin Karaye ya rushe majalisar masarautar sa

Published

on

Sarkin Karaye Alhaji Ibrahim Abubakar na biyu ya rushe majalisarsa bayan kammala wata ganawa da duk masu rike da mukamai a Masarautar.

Babban dan majalisar Sarkin Magajin Garin Karaye Injiniya Shehu Ahmad ne ya sanar da hakan, sai dai ya ce rushewar ba ta shafi wasu Hakimai guda takwas na Masarautar ba.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in yada labarai na karamar hukumar Karaye Haruna Gunduwawa ya fitar a yau.

An dakatar da hawan Sarki Majalisar masarautar Kano

An yi zangazangar kin amincewa da kara masarautu a Kano

Gwmantin Kano ta musanta yunkurin sauya wa sarkin Kano Masarauta

Sarkin Rano ya dakatar da wasu Hakimai

Sanarwar ta kara da cewa Sarkin ya jaddada aniyarsa ta fadada mukaman a cikin kananan hukumomi 8 na Masarautar, tare da alkawarta cewa wasu daga masu rike da mukaman za su dawo yayin da wasu kuma za a daga likkafarsu.

Ya kuma jinjinawa ‘yan majalisar ta sa bisa irin gudunmawar da suka bayar wajen ciyar da Masarautar ta Karaye gaba.

 

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!