Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

‘Yan sanda sun kara ceto yara biyu da aka sace a Anambra

Published

on

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Anambra ta cafke wasu mata 3 da aka samu da kananan yara guda biyu ‘yan kimanin shekaru 2 zuwa 4, an cafke matan ne a yankin kasuwar Nkpor/Tarzan Junction dake karamar hukumar Idemili ta arewa dake jihar Anambra.

Cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun kakakin rundunar ‘yan sanda ta jihar Anambra SP. Haruna Muhammad ta bayyana cewa izuwa yanzu dai basu kai ga gano asalin inda iyayen yaran suke ba, amma dai suna cigaba da bincike.

Shima a nasa bangaren kakakin rundunar ‘yan sanda ta jihar Kano DSP. Abdullahi Haruna Kiyawa ya bayyana Freedom Radio cewa rundunar ‘yan sanda ta jihar Anambra ta aiko musu da wannan bayani kuma suna kira ga al’umma ga duk wanda ya san wadannan yara to ya hanzarta ya tuntubesu.

Duba hotunan yaran a kasa:

RUBUTUKA MASU ALAKA:

Yadda hukumar Hisbah ta sauke ‘yan kwamitin gudanarwarta

Yaran Kano 9: Ganduje ya kafa kwamitin bincike na musamman

Ina yabawa ‘yan sandan jihar Kano –Magajin garin Daura

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!