Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Garin da ake aure akan naira dubu hamsin (N50,000) kacal a Kano

Published

on

Garin da ake aure akan naira dubu hamsin (N50,000) kacal a Kano

Dagacin garin Kera dake karamar hukumar Garko a nan Kano ya sanya dokar kayyade kudin aure da sadaki baki daya akan kudi N137,000 ga budurwa, bazawara kuma N50,000.

Kusan watannin uku kenan da dagacin Mallam Bello Musa ya sanya wannan doka, sai dai wasu daga al’ummar garin sun koka bisa wannan sabon tsari.

A zantawar da Freedom Radio ta yi da wasu iyaye a garin sun bayyana cewa ko kadan ba za su lamunci wannan tsari ba a don haka sun shirya tsaf domin kai kokensu gaban hukumar karbar korafe-korafe ta jihar Kano.

Haka kuma Freedom Radio ta tuntubi dagacin wanda ya bayyana cewa wannan doka fa sun yanketa ne domin samar da masalaha a garin, kuma al’umma da malaman garin duka sun amince da wannan doka.

Idan zaku iya tunawa dai a watan Janairu na shekara ta 2017 mahukunta a karamar hukumar Danbatta dake nan Kano, suma suka kaddamar da dokar kayyade aure sai dai ta samu cikas a karshe.

Rubutu masu nasaba:

Amarya ta haihu bayan wata hudu da Aure

An gurfanar da uba da ‘yarsa gaban kotu bisa zargin shirya auren bogi

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!