Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Hisba ta yi karin girma ga manyan jami’anta

Published

on

Hukumar Hisba ta jihar Kano ta daga likkafar wasu jami’anta biyar zuwa matsayin masu taimakawa babban kwamanda na hukumar.

Jami’an da suka samu karin girmar sun hada da Malam Yahya Alhassan da Malam Abubakar Salihu Muhammad da kuma Malam Aminu Abdu.

Sauran sune Malam Sabo Awaisu da Malam Abdulladif Buhari wadanda hukumar ta yaba da jajircewarsu wajen gudanar da aiki tare kuma da daga likkafarsu zuwa matsayi na gaba.

Hakan na cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun jami’in hulda da ja’ama na hukumar Lawan Ibrahim Fagge wanda kuma aka rabawa manema labarai.

Sanarwa ta kuma ce sababbin kwamandojin biyar za su jagoranci shiyoyi biyar da ke masarautun jihar ta Kano da suka hada da: Kano da Rano da Gaya da Karaye da kuma Bichi.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!