Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Manyan Labarai

Ya kamata Yan Najeriya su dakatar da zuwa asibiti kasashen waje-Buhari

Published

on

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayyana ‘’yan Najeriya a matsayin wadanda suka sha wahala sosai sakamakon cigaba da zuwa kasashen waje domin neman magani.

Shugaba Buhari ya bayyana hakan ne a Asibitin koyarwa na jamiar Alex Ekwueme ta gwamnatin tarayya dake Abakaliki lokacin kaddamar wa da mika kayan aiki ga hukumar Asibitin.

Shugaba Muhammadu Buhari wanda ya samu wakilcin ministan kimiyya da fasaha Dr Ogbonnaya Onu yace an kaddamar da ayyukan a Asibitin koyarwa na jamiar gwamnatin tarayya ta Alex Ekwueme ne domin magance matsalar zaizayar kasa.

Ogbonnaya Onu yace lokaci ya wuce da wani bangaren kasa za’a watsar da shi wajen gudanar da ayyuka sakamakon rashawa da ta yi katutu tsakanin al’ummar kasa .

Ministan na kimiyya da fasaha da ya wakilci Shugaba Buhari yace gwamnati ta damu kwarai da gaske game da lafiyar ‘’yan Najeriya.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!