Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

NAHCON ta karrama tashar Freedom Radiyo

Published

on

Hukumar aikin hajji ta kasa NAHCON ta karrama wakilin Freedom Radio a jihar Kaduna Abubakar Jidda Usman matsayin Dan Jarida mafi kwazo wajen kawo rahoton aikin hajjin da ya gabata.

A yayin wani bikin karramawa da kungiyar masu aike da rahotanni na aikin hajji masu zaman kan su suka shirya a birnin tarayya Abuja an baiwa hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kano lambar yabo kan hukumar da tayi fice wajen kula da kayan alhazai.

Kazalika an karrama hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kaduna matsayin wadda tayi fice wajen shirya aikin hajji.

Haka kuma an bada lambar yabo ga hukumar jin dadin alhazai ta birnin tarayya Abuja matsayin wadda tayi fice wajen samar da kyakykyawan masauki.
Sauran jihohin da suka samu lambobin yabo sun hada da Yobe, Kwara da kuma jihar Niger.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!