Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Ganduje zai dauki likitoci 44 a dukkanin kananan hukumomi

Published

on

Gwamnan Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana cewa, jihar za ta dauki likitoci aiki dai-dai daga kananan hukumomi 44 na jihar, don bunkasa yanayin kiwon lafiyar al’umma.

Gwamna Ganduje ya bayyana hakan ne yayin taron lafiya a matakin farko na shekarar 2020 da akayi jiya anan Kano.

Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya ce, a kokarin gwamnatin Kano na bunkasa harkokin kiwon lafiya a matakin farko, Gwamnatin jihar za ta sauya wajen da ma’aikatar hukumar kula da lafiya a matakin farko za su rika karbar albashi daga ma’aikatar kananan hukumomi zuwa hukumar bunkasa lafiya a matakin farko ta jiha.

Yayin da yake bude taron, ministan lafiya Dr. Osagie Emmanuel Ehanire ya ce gwamnatin tarayya na yin hobbasa wajen ganin tsarin lafiya a matsakin farko ya inganta, don su rika yin aiki awa 24 a kullum.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!