Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Kano ba ta bukatar kafa rundunar tsaro -Ganduje

Published

on

Gwamnan Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya ce, jihar ba ta bukatar kafa wata rundunar tsaro mallakin ta.

Gwamna Ganduje ya bayyana kuma jin dadin sa game da yadda jami’an tsaro ke gudanar da aikin su a jihar.

Wannan na cikin wata sanarwa da sakataren yada labaran gwamnan Kano Abba Anwar ya fitar jiya a nan Kano.

Sanarwar ta ce, Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana hakan ne lokacin da sabon mataimakin Sufeto Janar na yan sanda shiyya ta daya AlG Sadik Abubakar Bello ya kai masa ziyara gidan gwamnati.

A cewar sanarwar, gwamnan na Kano ya nuna gamsuwar sa bisa yadda jami’an tsaro ke gudanar da ayyukan su na tsaron lafiya da dukiyar al’umma, kasancewar wanzuwar hadin kai tsakanin hukumomin tsaro.

Abdullahi Umar Ganduje ya kara da cewa, shakka babu jihar Kano na amfani da sababbin na’urori na zamani da za su taimaka wajen dakile ayyukan batagari.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!