Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Al’ummar Tudun Murtala sun koka

Published

on

Gidauniyar cigaban Al’ummar unguwar Tudun Murtala sun yi kira da gwamnatin jihar Kano da ta kawo musu dauki akan hanyar su ta Tudun Murtala sakamakon lalacewar da hanyar tayi.

Shugaban gidauniyar Alhaji Yahaya Bagobiri yace al’ummar suna fama da matsalar hanya da matsalar rashin magudanar ruwa data tashi daga unguwar Gwagwarwa zuwa Tudun Murtala dake karamar hukumar Nassarawa.

Alhaji Yahaya Bagobiri ya bayyana hakan ne a ya yin taron da gidauniyar ta shirya don taya murna ga Sheikh Abdullahi Saleh Pakistan na jami’ar Al’qalam bisa zama Farfesa da yayi.

Labarai masu alaka:

Wasu ‘yan kasuwar Sabon gari sun koka kan yunkurin Uba Zubairu

Inda Ranka: ‘Yan kasuwa sun koka kan biyan harajin wuta mai hasken rana a Kano

Ya ce Sheikh Abdullah Saleh Pakistan ya dade yana bada gudunmuwar ilimin addinin Islama dana zamani a unguwar Tudun Murtala wanda hakan yasa al’ummar unguwar ba zasu taba mantawa da shi ba.

Da yake nasa jawabin a yayin taron Farfesa Abdullahi Saleh Pakistan bayyana farin cikin sa ya yi  bisa karramawar da jami’ar Al’qalam tayi masa da gidauniyar unguwar Tudun Murtala da sauran al’ummar unguwar baki daya.

Wakilin mu Shamsu Da’u Abdullahi ya rawaito cewa al’ummar unguwar sun kira ga masu kudin unguwar da su yi koyi da Sheikh Pakistan kan irin abin da yake yiwa al’ummarsa.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!