Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Musulmai su dinga aikata ayyukan alheri – Empathy Foundation

Published

on

Gidauniyar tausayawa da tallafawa mabukata wato Empathy Foundation ta ja hankalin al’ummar musulmi da su zage dantse wajen aikata ayyukan alkheri a wadannan kwanaki goma da muke ciki na zulhijja.

Shugaban kungiyar Mansur Musa Gabari ne ya bayyana hakan yayin da gidauniyar ta ziyarci gidan yara masu lalurar kwakwalwa ta ‘Torrey home’ dake unguwar Tudun Maliki da gidan kangararrun yara na Goron Dutse wato ‘Remand home’ da na masu lalurar yoyon fitsari don raba musu kayan abinci.

Mansur Musa Gabari ya kuma ce, yana da kyau masu wadata su rika tallafawa wadanda basu dashi musamman a lokutan salla.

Tun farko da take jawabi, shugabar gidan kula da yara masu lalurar kwakwalwa ta ‘Torrey home’ da ke unguwar Tudun-Maliki, Lauriya Sagir Garba, ta yabawa Gidauniyar ta Emphaty tare da bukatar masu hannu da shuni

Wakilin mu Abubakar Tijjani Rabi’u ya rawaito cewa, a yau gidauniyar ta Emphaty za ta ziyarci Dawakin Kudu don bayar da tallafin kwanan rufi ga wani masallaci da ruwan sama ya yaye rufinsa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!