Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

A ƙalla mutane kusan miliyan 3 rikici ya raba da gidajensu a Najeriya – majalisar ɗinkin duniya

Published

on

Hukumar kula da ƴan gudun hijira ta majalisar ɗinkin duniya (UNHCR) ta ce a ƙalla mutane miliyan 2 da dubu ɗari tara ne rikice-rikice da ke faruwa a Najeriya ya raba da gidajensu.

 

A cewar hukumar ta UNHCR akwai kuma mutane da ke zaune a sansanonin ƴan gudun hijira da suka kai 70, 000.

 

Babban jami’in hukumar da ke kula da yada labarai ta ƙetare Roland Schoenbauer da kuma jami’in yaɗa labaran hukumar anan Najeriya Gabriel Adeyemo sune suka bayyana haka yayin zantawa da manema labarai a shalkwatar hukumar da ke Lagos.

 

Sai dai hukumar ta yabawa Najeriya sakamakon yadda ta ce tana iya kokarinta wajen kula da ƴan gudun hijira wadanda suka shigo Ƙasar nan daga ƙasashe makwabta don neman mafaka.

 

Ya ce abin alfahari shine ganin cewa ƴan gudun hijira ana basu damar yin aiki ko neman ilimi da kuma kula da lafiya kamar yadda ƴan kasa ke da wannan dama.

Saboda haka hukumar ta bukaci ƙasashe mawadata da su taimaka wajen samar da isassun kudade da za ta ci gaba da gudanar da ayyukanta ba tare da samun matsala ba.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!