Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

A gaggauce: Ganduje ya bai wa mai buƙata ta musamman takardar ɗaukan aiki

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta bai wa wani Malami mai lalurar gani takardar ɗauka aiki kai tsaye.

Gwamna Dakta Abdullahi Umar Ganduje ne ya bai wa ma’aikatar ilimi ta jihar umarnin miƙa takardar ɗaukan aiki ga malamin.

Da yake bayyana amincewar sa da bada takardar ɗaukan aikin, gwamna Ganduje ya ce “A ƙoƙarina na inganta rayuwar al’umma, a madadin gwamnatin Kano na amince a baka takardar ɗaukan aiki ɓangaren koyarwa kai tsaye”.

Gwamnan ya bai wa Kwamishinan ilimi Muhammad Sanusi Sa’idu Ƙiru umarnin tura Dahuru Abdulhamid Idris zuwa makarantar masu buƙata ta musamman ta Tudun maliki domin ya ci gaba da koyarwa.

Tun da fari dai Malamin mai suna Dahuru Abdulhamid Idris na yin koyarwa ta sa kai wato Voluntery gabanin ba shi takardar ɗaukan aikin.

Wannan dai na cikin sanarwar da sakataren ƴaɗa labarai na gwamnan Abba Anwar ya fitar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!