Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnatin Kano ta fara nazari kan takardar musanta naɗin Ganduje a Farfesa

Published

on

Gwamnan Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya ce, yana nazarin takardar da jami’ar East Carolina (ECU) ta fitar wadda ta musanta ba shi matsayin Farfesa.

Mai bai wa gwamnan shawara kan yaɗa labarai Salihu Tanko Yakasai ne ya bayyana hakan ga Freedom Radio.

Yakasai ya ce, jami’ar ce ta aike wa gwamnan takardar naɗinsa a Farfesa da kuma ɗaukar aiki.

Jami’ar ta kuma sanya suna da hoton Gwamnan cikin malamanta, har ma ta wallafa hakan a babban shafinta na intanet inji Salihu.

Labarai masu alaka:

Ana kace-nace kan matsayin ‘Farfesa’ ga Ganduje

Siyasar Kano: PDP ta gargaɗi Ganduje kan cefanar da kadarorin gwamnati

Jaridar Premium Times ce dai ta samu wasiƙar musanta naɗin Gandujen a ranar Juma’a.

Jami’ar ta ce jami’inta ne ziƙau ya rubutawa Ganduje takardar naɗin, ba tare da ta samu amincewar hukumar jami’ar ba.

Sai dai Yakasai ya ce, yanzu haka gwamnati ta shiga nazarin takardar domin ɗaukar matakin da ya dace.

A ranar 1 ga Disamba ne sakataren yaɗa labaran gwamnan Malam Abba Anwar ya sanar da cewa an naɗa Ganduje Farfesa tare da ba shi aikin koyarwa a jami’ar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!