Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

A hukunta masu hannu a gobarar ofishin Akanta na kasa-Joe Odumakin

Published

on

Shugabar  cibiyar kawo Canji, wato  ‘center for change’ Dakta, Joe Okei- Odumakin,  ta bukaci gwamnatin tarayya da ta gufanar da wadanda aka kama suna da hannu wajen gobarar da ta tashi a ofishin Akanta  Janar na kasa.

Dakta , Joe Okel Odumakin ta bukaci hakan ne ta cikin sanararwar  da ta fitar a birnin Lagos, in da tace ya zama wajibi a kama tare da gurfanar da wadanda suka haddasa gobarar.

Labarai masu alaka.

A Yanzu -Yanzu : gobara ta tashi a Ofishin akanta na kasa

Gobara ta lalata dukiyoyi masu yawa a Kano

Kazalika Odumakin ta nemi Gwamnatin tarayya da ta gudanar da bincike don gano musababin gobarar.

Har ila yau shugabar cibiyar  ta ce kada Gwamnatin tarayya ta kyale batun gobarar ya tafi ba tare da an hukunta masu hannu a cikin laifin tashin ta ba.

A jiya Laraba  gobarar ta tashi a ofishin Babban Akanta na kasa, wanda kawo yanzu haka  ba’a san abinda ya haddasa ta ba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!