Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Abinda ya sanya malaman Najeriya suka dawo daga rakiyar Buhari

Published

on

Da alama Malaman addinin Musulunci a Najeriya sun soma dawowa daga rakiyar Gwamnatin Muhammadu Buhari sakamakon abin da suke cewa rashin mayar da hankali wajen magance matsalar tsaro da ta addabi musamman Arewacin kasar.

Malamai da dama da BBC ta tattauna da su sun ce dole gwamnatin Shugaba Buhari ta zage damtse don shawo kan matsalar tsaron ƙasar idan ba haka ba Allah zai yi fushi da ita.

Wannan jan kunne na zuwa ne bayan waɗanda ake zargi mayaƙan Boko Haram ne sun kashe aƙalla manoma 43 a jihar Borno da ke arewa maso gabashin ƙasar.

Malam Aminu Ibrahim Daurawa, fitaccen malamin da ke jihar Kano, ya shaida BBC cewa ya zama wajibi Shugaba Buhari ya sauya salo wajen tunkarar matsalar tsaron da ke addabar arewacin ƙasar.

Ya ƙara da cewa: “Waɗannan abubuwa guda uku yanzu sun ƙara tabarbarewa sun lalace a wannan kasa” don haka ya zama wajibi a shawo kansu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!