Connect with us

Labarai

ACF ta karyata bidiyon da ke cewa ta na goyon bayan yi wa yan ta’adda afuwa

Published

on

Kungiyar tuntuba ta Arewa ACF, ta karyata wani faifan bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta wanda ke zargin ta da goyon bayan yi wa ’yan ta’adda da ’yan bindiga afuwa.

Ta cikin wata sanarwa da ta fitar, kungiyar ta ce maganganun sun samo asali ne daga wata hira da Wazirin Dutse, Alhaji Bashir Dalhatu, ya yi, amma aka yanke ta kuma an fassara ta ba dai-dai ba domin cimma wata manufa.

ACF ta bayyana cewa Alhaji Dalhatu ya yi jawabi ne inda ya yi Allah-wadai da ta’addanci, ya kuma yi kira da a kawar da ’yan ta’adda cikin gaggawa.

Kungiyar ta ce bai taba kiran a yi wa ’yan ta’adda afuwa ba, kuma misalin shirin afuwar Yankin Niger Delta da ya ambata shi ne wajen nuna cewa gwamnati na iya amfani da duk wata hanya ta magance matsalar tsaro.

A ƙarshe, ACF ta ce bata taɓa goyon bayan afuwa ga ’yan ta’adda ko ’yan bindiga ba, kuma ta yi watsi da duk wani jita-jita da ke cewa tana marawa irin wannan magana baya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!