Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

AFCON 2021: Sierra Leone ta gayyaci ‘yan wasa 16

Published

on

Mai horas da kungiyar kwallon kafa ta Sierra Leone John Keister ya gayyaci ‘yan wasan kasar 16 dake taka leda a kungiyoyi daban-daban a fadin duniya don buga wasan da zasu fafata da Najeriya a mako mai zuwa na neman tikitin gasar cin kofin Afrika na 2021.

Leone Stars dai zasu kara da Super Eagles a ranar Juma’a 13 ga watan Nuwamba a filin wasa na Samuel Ogbemudia dake birnin Benin a jihar Edo, kafin itama ta karbi bakuncin Najeriya bayan kwanaki hudu da kammala wannan wasan.

Leone Stars ta zo ta hudu a rukunin L da maki daya a wasanni biyu, yayin da Super Eagles take kan gaba da maki shida a wasanni biyun farko.

Kuma idan Najeriya ta yi nasara a wasannin biyu kai tsaye zai bata damar samun tikitin zuwa gasar.

AFCON: Najeriya ta gayyaci ‘yan wasa 24

AFCON 2021: Za’ai wasan Najeriya da Sierra Leone ba ‘yan kallo

‘Yan wasan da Keister ya gayyata sun hada da Osman Kakay daga Queens Park Rangers a Ingila da Mustapha Dumbuya daga Tampa Bay Rowdies a Amurka da Alie Sesay daga Zira FK a Azerbaijan da Kwame Queen daga Vikgur Reykjavik a Iceland da Mohamed Medo daga Kamara FC Haka a Finland da Kelvin Wright daga Orebro a Sweden da George Davies daga Austria da Mohamed Turay daga China da kuma Mustapha Bundu daga Belgium.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!