Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

AFN Crisis: Kowane shugaban tsagin bangarorin biyu zai gudanar da zabensa da ban

Published

on

Rikicin shugancin hukumar wasannin guje-guje da tsalla-tsalle ta kasa AFN, na kara kamari yayin da kowane tsagin bangarorin biyu ke shirin gudanar da zabe a yau Litinin 14 ga watan Yuni.

Yayin da masu ruwa da tsaki a hukumar dake goyon bayan shugaban daya bangaren Inginiya Ibrahim Shehu Gusau za su gudanar da zabensu a jihar Kebbi.

Haka kuma, suma daya tsagin bangaren da shugaba Hon. Olamide George ke jagoranta dake samun goyon bayan ma’aikatar wasanni ta kasa za su gudanar da nasu zaben a Abuja.

A kwanakin baya ne hukumar wasan gudu da tsalle-tsalle ta duniya tare da mambobin hukumar AFN suka gudanar da taron kwanaki biyu don yin sasanci tsakanin bangarorin biyu, inda aka cimma matsayar gudanar da zabe a ranar 14 ga watan Yuni a yunkurin kawo karshen rikicin.

Yanzu haka dai masu ruwa da tsaki na cigaba da sanya ido domin ganin yadda sakamakon zaben guda biyu za su kasance.

 

AMM

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!