Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Akwai bukatar sauya salon yaki da rashawa a Najeriya – Osinbajo

Published

on

Mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo ya bayyana cewa akwai bukatar Najeriya ta canja salon yadda take fuskantar yaki da cin hanci da rashawa a kasar.

Mataimakin shugaban kasa Osinbajo ya yi wannan bayani ne a ranar Talata wajen bikin yaki da cin hanci da rashawa da sauran laifukan da suka dangance su a yankin Afirka karo na 20 da aka gudanar ta intanet.

Bikin na bana da aka yiwa taken, ‘Sabbin dabarun magance cin hanci da kuma harkokin kudi ba bisa ka’ida ba’ ya zo ne a dai-dai lokacin da ake gudanar da bincike kan shugaban hukumar yaki da masu yiwa tattalin arzikin kasa zagon kasa, Ibrahim Magu kan zargin rashawa.

Ya ce babu wani siddabarun da za a iya yi don kawo karshen cin hanci da rashawa da kuma batar da sawun kudaden haram ko kuma kwato kadarorin da aka mallaka da kudin da aka samu ta hanyar cin hanci da rashawa.

Osinbajo ya ce abin yi kawai shine a dage da yin aiki tukuru tare da jajircewa sai an kai ga nasarar magance matsalar.

Ya kara da cewa dole ne a tabbatar da cewa an mayar da harkar cin hanci da rashawa abu mai matukar tsadar gaske ga dukkan wadanda ke da alaka da shi tare kuma da aikewa da kakkausan sako ga irinsu cewa harkar rashawa fa ba riba a cikinta.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!