Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Amarya ta rasu ana dab da bikinta

Published

on

Wata matashiyar amarya mai suna Atika Isah yar asalin unguwar Sunusi dake jihar Kaduna ta rasa ranta a yayin da ake dab da fara shirye-shiryen bikin aurenta.

Ranar 31 ga watan Janairun da muke ciki ne aka sanya domin daura auren marigayiyar da angonta mai suna Engr. Nura Yahuza, kamar yadda kuke gani a katin daurin auren dake kasa.

Sai dai cikin ikon Allah amaryar ta rasa ranta sakamakon gajeruwar rashin lafiya a daren jiya Lahadi.

Shima a nasa bangaren angon ya wallafa a shafinsa na Facebook cewa

 

Tuni dai akayi jana’izar marigayiyar kamar yadda musulunci ya tanada a masallacin jumu’a na Usman Dan Fodiyo dake unguwar Sanusi a jihar Kaduna.

Idan zaku iya tunawa dai ko a karshen shekarar da ta gabata wata amarya ta rasa ranta, a yayin da take tsaka da rabon katin bikinta, sanadiyyar hatsari a babur mai kafa uku wato a dai-daita sahu (Napep) sakamakon ruwan sama da aka tafka a unguwar Rigasa dake jihar ta Kaduna.

Kazalika a watan Disamba na shekarar 2019 da ta gabata wata amarya ta rasa ranta, sakamakon fadawa rijiya a rashin sani, yayin da ake tsaka da shagalin bikinta a karamar hukumar Danbatta dake nan Kano.

Labarai masu alaka:

Amarya ta haihu bayan wata hudu da Aure

Garin da ake aure akan naira dubu hamsin (N50,000) kacal a Kano

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!