Connect with us

Ƙetare

Ambaliyar ruwa ta hallaka mutane 47 tare da lalata fiye da gidaje 56,000 a Nijar

Published

on

Hukumomi a kasar Nijar sun ce ambaliyar Ruwa ta hallaka mutame 47 tare da raba fiye da mutum 56,000 da gidajensu a Jamhuriyar Nijar.

 

Ambaliyar ta shafi gidaje 7,754 a cikin unguwanni da ƙauyuka 339, in ji hukumar tsaron fararen hula ta ƙasar.

 

Wasu mutane 30 sun mutu bayan gidajensu sun rushe yayin da mutne 17 suka nutse a ruwa.

 

Haka kuma, a cewar hukumar, ambaliyar ta raunata mutum 70 ta kuma haddasa mutuwar dabbobi 257.

 

Sai dai, Kwamiti na ƙasa da aka ɗora wa alhakin hana ambliya ya ce ya fara raba tallafin abinci ga iyalai 3,776.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!