Connect with us

Labarai

An boye daliban Kagara a Birnin Gwari – Matawalle

Published

on

Gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle ya ce dalibai da ma’aikatan Kwalejin Kimiyya da ke Kagara a jihar Neja da ’yan bindiga suka sace a ranar Laraba da ta gabata suna tsare a Birni Gwari dake jihar Kaduna tare da wadanda suka sace su.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a shirin Talabijin na Channels yana mai tabbatar da cewa nan ba da jimawa ba za a saki wadanda aka sace.

Matawalle ya yi zargin cewa akwai hadin kai daga masu ruwa da tsaki wajen aikata miyagun laifi, wanda shi ne ya ke bai wa yan ta’addar nasara a cikin ayyukan da suke yi na ta’addanci a ƙasar nan.

A cewarsa, batun tsaro na bukatar karin himma daga dukkan masu ruwa da tsaki musamman na magance matsalolin ayyukan yan Boko Haram da masu garkuwa da mutane.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!