Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kasuwanci

An cimma matsaya tsakanin gwamnati da kamfanin Twitter

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ce, kamfanin Twitter ya amince da dukkanin sharuɗɗan da ta gindaya masa gabanin ci gaba da gudanar da ayyukan sa a Najeriya.

Ƙaramin ministan ƙwadago da samar da aikin yi Festus Keyamo ne ya sanar da hakan, a wata hira da gidan Talabijin na Channels ya yi da shi a ranar Lahadi.

Festu Keyamo wanda guda ne daga cikin mambobin kwamitin da gwamnati ta samar da zai nazarci ayyukan kamfanin na Twitter tun a ranar 4 ga watan Yunin shekarar da muke ciki.

A cewar Festus Keyamo, kwamitin na samun ci gaba a tattaunawar da yake yi da kamfanin na ganin an daidaita.

Idan za a iya tunawa an dakatar da kafanin ne sakamakon goge wani rubutu da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi a shafin sa.

 

Solacebace:

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!