Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Buhari ya amince da bukatar tattaunawa da kamfanin Twitter

Published

on

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da bukatar tattaunawa da kamfanin Twitter ya bukata kan batun dakatar da ayyukan sa a Najeriya.

Shugaba Buhari ya bada umarnin hada wata tawaga da za ta hada da Ministan yada labarai da raya al’adu Alhaji Lai Mohammed wanda shi ne zai jagoranci tawagar don tattaunawa da kamfanin.

Cikin tawagar sun hada da ministan shari’a kuma Atoni Janar na kasa Abubakar Malami, da ministan sadarwar da bunkasa tattalin arziki Dr Isah Ali Ibrahim Pantami da kuma ministan harkokin kasashen waje Geoffrey Onyema.
Sauran su ne: ministan ayyuka da gidaje BabaTunde Raji Fasola da kuma karamin ministan kwadago da samar da aikin yi Festus Keyamo, da sauran manyan ma’aikatan gwamnati.

Tuni dai kamfanin Twitter ya ce a shirye yake don tattaunawa da gwamnatin kan dakatar da shi daga ayyukan su a Najeriyar.

Dakatarwar dai ta biyo bayan goge wani rubutu da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya wallafa a shafinsa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!