Connect with us

Labarai

An dage sauya shekar Gwamna Abba zuwa 12 ga Janairu

Published

on

Rahotannin da ke cewa Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, zai fice daga jam’iyyar NNPP zuwa jam’iyyar APC an dage shi, kamar yadda jaridar PlatinumPost ta rawaito.

 

A cewa wasu majiyoyi masu tushe na kusa da gwamnan sun bayyana cewa ranar da aka fara tsara wa domin sauyin sheƙar a hukumance, wato Litinin, 5 ga Janairu, 2026, yanzu an sauya ta zuwa Litinin, 12 ga Janairu, 2026.

 

A baya, jaridar Daily Nigerian ta rawaito cewa Gwamna Yusuf zai sauya sheƙa zuwa APC a ranar 5 ga Janairu.

 

Sai dai wata majiya mai tushe, wadda ta nemi a sakaya sunanta kuma ta halarci wani taro tsakanin Gwamna Yusuf da Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, a Abuja ranar Juma’a, ta bayyana cewa gwamnan ya nemi ƙarin lokaci.

 

A cewar majiyar, Yusuf na son ci gaba da tuntubar wasu ‘yan majalisar dokokin jihar da sauran manyan masu ruwa da tsaki da har yanzu ba su bayyana cikakken goyon bayansu ga wannan yunƙurin siyasa ba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!