Connect with us

Ƙetare

An dakatar da zirga-zirga a sararin samaniyar Dubai

Published

on

Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE) ta dakatar da hawa da saukar jirage a Birnin Dubai biyo bayan wani harin da aka kai daga Iran. Wannan mataki ya zo ne domin tabbatar da tsaro a sararin samaniyar birnin.

 

Kamfanin jirgin sama na Emirates ya sanar da dakatar da zirga-zirgar jiragen sama da ke zuwa Dubai har sai nan da wani lokaci. Kamfanin ya ce wannan mataki zai baiwa jami’an tsaro damar gudanar da bincike da kuma tabbatar da lafiyar fasinjoji.

Haka zalika, rufe sararin samaniyar ya shafi kasashen yankin da dama, inda hukumomin zirga-zirga na sama suka bayar da sanarwar hana wasu jirage sauka ko tashin sama a Dubai har sai an sami kwanciyar hankali. Wannan mataki na nuna yadda rikicin na Iran ke shafar zirga-zirgar jiragen sama a duniya baki ɗaya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!