Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

An gano yara 273 dake zaman kansu a Kano

Published

on

Kungiyar tabbatar da tsaro da zaman lafiya da ake kira da Nigerian Peace Unity Progress reshen jihar Kano ta bayyana cewa ta samu nasarar ceto kananan yara guda 273 dake rayuwa a kasuwannin jihar Kano.

Babban kwamandan kungiyar ta jihar Kano Ibrahim Adam Isah ya bayyana hakan a yayin taron daga likkafar wasu jami’an rundunar da ya gudana yau lahadi a nan Kano.

Ibrahim Adam ya bayyana cewa bisa binciken da suka gudanar sun gano yadda yaran ke rayuwa ta zaman kansu a kasuwannin Kantin wari, Kasuwar Kofar Wambai da kuma Kasuwar Sabon Gari da kuma wasu sassa na jihar Kano, ba tare da sahalewar iyayen su ba.

Kazalika Ibrahim Adam ya kara da cewa yara 27 ne kacal daga cikin 273 ‘yan asalin jihar Kano, yayin da sauran kuma suka shigo Kano daga makwabtan jihohi, har ma da wasu kalilan daga kasashe makwabtan Najeriya.

Yayin da kwamandan kungiyar ta jihar Kano Ibrahim Adam Isah ke jawabi.

Tuni dai kungiyar tare da hadin gwiwar hukumomin tsaro suka mika kananan yaran ‘yan jihar Kano zuwa ga iyayensu, sa’annan kuma sauran yaran aka mika su zuwa ga gwamnatocin jihohinsu.

Har ila yau, taron na kungiyar ta Nigerian Peace Unity Progress dai ya samu halartar iyayen kungiyar da suka hadar da dagatai da kuma jami’an ‘yan sanda, da lauyoyi masana shari’a.

Labarai masu alaka:

Ilimin ‘ya’ya mata zai gyara rayuwar al’umma –Yariman Kano

Kano9: Ina rokon mahukunta su magance satar yara -Sheikh Kariballah Kabara

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!