Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

An kama ‘yan fashi da makami a jihar Nasarawa

Published

on

Jami’an rundunar ‘yan sanda dake aikin sintiri na jihar Nasarawa sun kama wasu da ake zargin ‘yan fashi da makami ne da satar mutane su 27.

Kwamishinan ‘yan sanda na jihar ta Nasarawa Bola Longe ya sanar da hakan ga manema labarai cewa an kama ‘yan fashin ne a wurare daban-daban cikin makwanni biyu da suka wuce.

Yayin da yake holan ‘yan fashin a shalkwatar rundunar dake birnin Lafia a jihar Nasarawa, Bola Longe ya ce daga cikin wadanda aka kama akwai wadanda suka kashe shugabanni al’ummar Odu wato Amos Obere.

Kwamishinan ‘yan sandan ya yi bayanin cewar, an kama wadanda ake zargin a wata mashaya ya yin da suke tsaka da holewa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!