Connect with us

Ƙetare

An kawo ƙarshen tattaunawar da aka yi tsakanin Rasha da Ukraine

Published

on

An kawo ƙarshen tattaunawar da aka yi tsakanin Rasha da Ukraine

 

 

An kawo ƙarshen tattaunawar da aka yi a baya bayan nan tsakanin Rasha da Ukraine a Istanbul ba tare da an fitar da wata muhimminiyar sanarwa ba.

 

Rahotonni sun bayyana cewa, bangarorin biyu sun ce sun amince da yin aiki tare wajen sake yin musayar fursunoni na sojoji da na farar hula.

 

Masu shiga tsakani na Ukraine sun ce, babu wata yarjejeniya da aka cimma a tattaunawar tsakanin ƙasashen biyu amma Kyiv a shirye ta ke ta tsagaita wuta a yanzu.

 

Sai dai rahotonni sun bayyana cewa, fadar Kremlin ta sha yin watsi da fatan samun gagarumin ci gaba, tana mai cewa bambancin da ke tsakanin ɓangarorin biyu suna da yawa don haka zai yi wuya a iya cimma yarjejeniyar zaman lafiya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!