Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

An rantsar da shugaba Bassirou Diomaye Faye na Senegal

Published

on

An rantsar da zababben shugaban kasar Senegal, Bassirou Diomaye Faye, a matsayin shugaban kasar na biyar, yayin wani katafaren biki a babban birnin kasar Dakar.

Shugabannin kasashen duniya da dama ne suka halarci bikin rantsarwar da suka hada da shugaban Najeriya kuma jagoran kungiyar tattalin arzikin kasashen Afirka ta yamma, Ecowas, Bola Ahmed Tinubu.

Faye ya yi nasara da kaso 54 cikin dari na kuri’un da aka kada a zaben da aka jinkirta a kan abokin hamayyarsa na hadakar jam’iyyu masu mulki.

A ranar Juma’a ne Kotun Kolin kasar ta yammacin Afirka, ta tabbatar da Faye a matsayin wanda ya ci zaben na ranar 24 ga watan Maris 2024.

Kafin a kai ga zaben, kasar ta yi fama da tarzoma daban-daban bayan da Shugaba Sall ya yi yunkurin jinkirta zaben.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!