Connect with us

Labarai

An rufe wuraren taron bukukuwa a jihar Kano sakamakon fara Azumi

Published

on

Hukumar Tace Fina-finai ta Jihar Kano ta ba da umarnin rufe dukkan wuraren nishaɗi a jihar nan take, ciki har da gidajen gala da na casu da na tarukan biki.

 

A cikin wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman ya fitar a ranar Talata, umarnin zai fara aiki daga ƙarfe 10:00 na dare a ranar Laraba, 18 ga Fabrairu, 2026, kuma zai ci gaba da aiki har zuwa ƙarshen watan Ramadan mai alfarma.

 

Hukumar ta bayyana cewa an ɗauki wannan matakin ne don bai wa mazauna jihar damar yin azumin Ramadan cikin salama da kuma gabatar da ayyukan addini cikin yanayi na natsuwa da kwanciyar hankali.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!