Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

An samu raguwar masu cutar Corona a ranar Alhamis

Published

on

Hukumar dakile cututtuka masu yaduwa ta kasa NCDC ta sanar da samun sabbin masu dauke da cutar COVID-19, 182 a jihohi 15 na kasarnan da birnin tarayya Abuja.

Hukumar ta wallafa hakan ne a daren Alhamis ta shafinta na Twitter.

NCD ta kamar kullum jihar Legas ce ke kan gaba wajan adadin mafi yawa na wadanda suka kamu da cutar da mutane -111babban burinin tarayya Abuja ta samu mutane -16 jihar Akwa Ibom mutane-10, jihar Oyo mutane-8.

Jihohin Kaduna da Delta na da mutane 6-6 yayin da jihar Rivers keda mutane-5, jihohin Ogun da Ebonyi mutane 4-4 suka kamu jihar mutane Kano-3 jihohin Plateau da  Gombe da kuma Kwara mutane 2-2 suma jihohin Kebbi da   Bauchi da  Borno mutum 1-1.

Mutane 8,915 suka kamu da cutar a sassan kasar nan daban daban.

Daga ciki mutane 2,592 sai kuma mutane 259 da cutar ta hallaka.

Adadin mutum 182 da aka samu a ranar Alhamis shine adadi mafi karanci cikin kwanaki 12 da suka wuce inda a kullum ake samun masu dauke da cutar sama da 200 a kasar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!