Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Tambuwal zai gana da Buhari kan harin ‘yan ta’adda a Sokoto

Published

on

Fadar shugaban kasa ta shirya ganawa tsakanin Shugaba Muhammadu Buhari da gwaman jihar Sokoto Aminu Waziri Tambuwal kan kazamin harin da aka kai a daren ranar Laraba wanda ya shafi wadanda ba su ji ba ba su gani ba, a yankin kudu maso gabashin jihar ta Sokoto.

Gwamnan Sokoto Aminu Waziri Tambuwal ne ya bayyan hakan ta cikin wata sanarwar da mai baiwa gwamnan shawara kan kafafan yada labarai Muhammad Bello ya sanya wa hannu.

Sanarwar tace gwamnan ya jajantawa al’ummar da harin ya shafa sannan gwaman ya baiwa hukumar bada agajin gaggawa ta jihar SEMA umarnin ta ziyarci wurin da aka kai harin domin tan-tance irin barnar da aka aikata da kumar samar da kayan jin kai ga mutanen da harin ya shafa.

Tambuwal ya shaidawa masu rike da masarautun gargajiya da masu ruwa da tsaki na yankin cewa bayan tattaunawa tsakanin jiya da yau da fadar shugaban kasa ya samu gayyata domin ganawa da shugaban kasa domin shawo kan alamarin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!