Connect with us

Ƙetare

An tilasta wa jirgin sojin saman Najeriya sauka a Burkina Faso- Mahukunta

Published

on

Gwamnatin Burkina Faso ta ce an tilastawa wani jirgin saman sojin saman Najeriya , da ke ɗauke da sojoji 11 sauka a ƙasar a ranar Litinin bayan da aka ce ya keta sararin samaniyar ƙasar ta.

Wata sanarwa da ta fito daga gwamnatin ƙasar ta ce jirgin sojan na ɗauke da ma’aikata biyu da fasinjoji tara a cikin sa kuma dukkansu jami’an soji ne, da binciken da hukumomin ƙasar Burkina Faso suka gudanar ya nuna cewa jirgin ba shi da izinin shawagi a sararin samaniyar ƙasar.

Ƙungiyar AES ta yi alla-wadai da lamarin tare da kakkausan suka  kan keta  sararin samaniyar duk wata ƙasa da ke cikin ƙungiyarta.

Haka kuma Ƙungiyar, ta yi gargaɗin ɗaukar mataki kan duk wani jirgi da ya keta sararin samaniyar duk wata ƙasa da ke yankin da tare da izini ba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!