Connect with us

Ƙetare

Ana ci gaba da kokarin zakulo mutanen da suka makale bisa ruftawar Mahakar ma’adanai a Ghana

Published

on

Hukumomi a kudancin kasar Ghana, sun ci gaba da aikin ceto wasu masu haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba da ake fargabar sun makale a ƙarƙashin wata mahaƙa da ta rufta a Larabar makon nan.

 

An tabbatar da mutuwar mutum uku, yayin da wani mutum guda ke kwance a asibitin cikin mawuyacin hali, bayan ruftawar mahaƙar da ke ƙauyen Akyem Wenchi a gundumar Denkyembour a yankin gabas.

 

Jamai’a na cewa ana fargabar cewa akwai mutum 30 da suka maƙale bayan rufawar mahaƙar.

Kawo yanzu ba a san dalilin da ya haifar da ruftawar mahaƙar ba.

 

Jami’an tsaro sun fice daga yankin, bayan da wasu fusatattun matasa da mazauna yankin suka mamaye mahaƙar a lokacin da ake aikin ceton.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!