Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Zabtarewar kasa ta yi sanadiyyar mutuwar mutum 50 a Myanmar

Published

on

Akalla mutane 50 ne suka mutu bayan zabtarewar kasa a wani wuri da ake hakar ma’adanai a arewacin Myanmar, a cewar hukumomin kaasr.

Lamarin wanda ya auku da safiyar ranar alhamis ya faru ne a yankin Hpakant da ke jihar Kachin bayan ruwan sama mai yawa, in ji ma’aikatar kashe gobara ta Myanmar.

Sanarwar ta ce, laka ta lullube masu hako ma’adanai, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar mutane 50.

Ma’aikatar ta ce har yanzu ana ci gaba da aikin ceto mutanen da kasa ta rufe, kamar yadda ta bayyana a shafinta na Facebook.

Hotunan da aka sanya a shafin Facebook sun nuna yadda masu aikin ceto ke aikinsu cikin laka.

Zaizayewar kasa ko kuma laka ba sabon abu ne ba a yankin, na mutanen da ke fama da tsananin talauci yayin da suke neman abinda za su ci.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!