Connect with us

Labarai

Ana gudanar da zanga-zangar neman inganta rayuwar yan sanda a Abuja

Published

on

Ana ci gaba da gudanar da zanga-zangar neman inganta rayuwar yan sandan Najeriya a birnin tarayya Abuja.

 

 Dan gwagwarmayar nan kuma tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa Omoyele Sowore, ne ya jagoranci gungun masu zanga-zangar.

 

Masu gudanar da wannan zanga-zanga, sun bukaci gwamnati ta duba halin kuncin da ‘yan sanda ke fuskanta, musamman yadda albashinsu ke ƙasa da kima, tare da rashin kula da ‘yan sanda da suka yi ritaya. 

 

Haka kuma, sun ce, lokaci ya yi da za a mutunta waɗanda ke bayar da rayukansu don kare lafiyar jama’a da dukiyarsu.

 

Sowore ya bayyana cewa, “Yan sanda su ne ginshiƙin tsaro a ƙasa, amma ana wulaƙanta su da iyalansu. 

 

Ya kuma ce ba za su ci gaba da shiru ba alhali suna rayuwa cikin talauci bayan shekaru da dama na hidima.

 

Masu zanga-zangar sun rike kwalaye masu ɗauke da rubuce-rubuce kamar:

 

“A biyan ‘yan sanda albashi mai kyau yanzu!”

 

“Rayuwa mai kyau ga masu ritaya!”

 

“’Yan sanda ma mutane ne!”

 

Zanga-zangar na gudana ne cikin lumana, tare da jami’an tsaro da suka tabbatar da zaman lafiya a wajen.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!