Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ana wata-ga-wata: Buhari ya kara farashin man fetur zuwa 212

Published

on

Hukumar kayyade farashin man fetur ta kasa (PPPRA) ta kara farashin man fetur zuwa naira dari biyu da goma sha biyu da kobo shida.

A cikin wata sanarwa da hukumar ta PPPRA ta fitar a daren jiya, ta ce yanzu litar man za a rika sayar da ita ne akan naira dari biyu da goma sha biyu.

Sanarwar ta ce a yanzu tataccen man fetur yana isowa kasar nan ne akan naira dari da tamanin da tara da kobo sittin da daya, yayin da farashin dapo-dapo ake sayarwa akan naira dari biyu da shida da kobo arba’in da biyu.

Wannan na zuwa ne kwanaki kadan bayan sanarwar da kamfanin mai na kasa NNPC ya yi, wanda ya ba da tabbacin cewa ba za ayi karin farashin mai a watan Maris ba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!