Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ana zargin likita da sanadin mutuwar mara lafiya

Published

on

Ana zargin asibitin WISDOM mai zaman kansa a Nassarawa GRA da yiwa wani mara Lafiya tiyata tun kafin sakamakon da zai nuna za’a iya yi masa aikin ko kuwa a’a ya fito.

Daya daga cikin ‘yan uwan marigayi mai suna Bashir Hassan ya ce mamacin na fama da ciwon sukari ne wanda ya taba masa kafa har ta kai sai an yanke ta, don haka aka tura su su yi gwajin jini da sauran gwaje-gwajen da zasu nuna cewa za’a iya yi masa aikin ko kuma a’a.

Amma sun tafi yin gwaje-gwajen kafin su dawo sai suka tarar sun yi masa aikin har ya rasu likitan kuma ya Gudu.

AKTH ya samu nasarar gudanar da aikin kwakwalwa karo na biyu

Gwamnatin tarayya ta shaidawa ma’aikatan lafiya muradinsu ba mai yiwuwa bane

Kungiyar Likitoci reshen Jihar Ondo sun bayyana bukatun yajin aikin JOHESU da cewar hankali ba zai dauka ba

‘Yan uwan mamacin sun kuma sheda cewar saida suka bukaci su ajiye Naira dubu dari da Ashirin 120’000 a matsayin kudin kafin alkalami.

Yayin da suka nemi su bada Naira dubu tamanin 80,000 hukumomin asibitin suka ki saida su basu gaba ki daya.

Ko da muka tuntubi Shugaban asibitin Dr, Ujudu Pitters ya ce yanzu ana kan buncike ba zai  ce komai ba kan batun.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!