Connect with us

Labarai

Jigawa: Yan sanda sun fara bincike kan rasuwar dattijo a dakin Otal

Published

on

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Jigawa ta fara bincike kan mutuwar ba-zata da aka samu a wani otal da ke cikin birnin Dutse, yana yin da zama akwai zargi.

 

A ranar Talatar nan 21 ga Yuli wannan shekara ta 2026 namacin, mai shekaru 60, ya shiga otal ɗin tare da wata budurwa mai shekaru 20, kuma bayan ya nemi a kawo masa abinci sai ya fara fama da matsananciyar wahalar numfashi.

 

Da samun rahoton ne Rundunar ta tura jami’an ta na Sashen Yalwawa cikin gaggawa tare da garzayawa da mutumin zuwa babban Asibitin Dutse, inda likitoci suka tabbatar da rasuwarsa bayan yan gwaje-gwaje.

 

Tini dai Jami’an dake bincike suka killace wurin da abin ya faru tare da gudanar da bincike kan abinci da abubuwan sha, ciki harda wani sinadari da ake zargin na ƙara ƙarfin jima’i ne, da wasu kayayyakin marigayin domin ci gaba da bincike.

 

A cewar Rundunar bayan an kammala duk matakan da suka dace, an miƙa gawar mamacin ga iyalansa domin yi masa jana’iza bisa ga buƙatarsu, ya yin da Budurwar da ke tare da shi a lokacin da ya faru ke ci gaba da baiwa jami’an dake bincike haɗin kai ta hanyar bayar da bayanan da za su taimaka wajen aikin da suke.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!