Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Siyasa

APC zata yi bincike kan zargin da akewa shugaban ta na kasa

Published

on

Kwamitin gudanarwar jam’iyyar APC na kasa ya kafa kwamitin ladaftarwa mai kunshe da mutum biyar wanda zai bincike zarge-zargen da mataimakin shugaban jam’iyyar na kasa mai kula da jihohin arewa Sanata Lawan Shu’aibu, ya yi ga shugaban jam’iyyar na kasa Adams Oshimhole.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun sakataren yada labaran jam’iyyar na kasa Lanre Isa-Onilu.

Sanarwar ta ce, kwamitin ladaftawar mai kunshe da mutum biyar zai bincika ya gani ko akwai kanshin gaskiya cikin zargin da Sanata Lawan Shuaibu ya yi na cewa shugaban jam’iyyar Adams Oshimhole, ba ya biyayya ga matakai da kwamitin gudanarwar jam’iyyar ya amince da shi.

A jiya Alhamis ne dai kwamitin gudanarwar jam’iyyar APC na kasa, ya kada kuri’ar amincewa da shugabanci Adams Oshimhole a yayin taron da ya gudanar karo na talatin da takwas

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!