Connect with us

Labarai

Arewa na da kwararrun da za su magance matsalolin yankin- Uba Sani

Published

on

Gwamnan Kaduna, Uba Sani, ya bayyana cewa, yankin Arewacin Nijeriya na da kwararru da hazikan Mutane da za su iya magance matsalolin rashin ci gaba da ake fama da su, muddin manyan yankin suka haɗa kai domin tafiyar hanya ɗaya.

Gwamnan ya bayyana haka ne lokacin da shugabancin Arewa Consultative Forum ACF, ƙarƙashin jagorancin Alhaji Bashir Dalhatu, ya kai masa ziyara a Kaduna.

Ya ce lokaci ya yi da Arewa za ta tashi tsaye don ta yi aiki wajen warware talauci, gibin ilimi da matsalolin lafiya da suka daɗe suna damun yankin.

Gwamnan ya jaddada cewa Arewa na da dubban kwararru a fannonin kasuwanci, harkokin lafiya, masana’antu, karatu da kirkire-kirkire, waɗanda ake buƙatar haɗa su a wuri ɗaya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!