Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Matawalle ga ‘yan kudu: Idan ‘yan arewa suka kai harin ramuwa ba za mu iya kareku ba

Published

on

Gwamnan jihar Zamfara Bello Muhammed Matwalle ya yi gargadin cewa al’ummar arewa za su iya mai da martani matukar aka ci gaba da kashe ‘yan yankin a kudancin kasar nan.

Ya kuma bukaci takwarorin-sa na kudu da su dakatar da faruwar lamarin don gudun harin daukar harin ramuwa a arewa.

Gwamnan na Zamfara ya bayyana hakan ne ta cikin wata sanarwa da ya fitar a daidai lokacin da kungiyar dattijan arewa ta ACF ta fitar da makamancin sanarwar da ke sukar shugabannin kudanci kan shiru da su ka yi ana kashe al’ummar arewa a yankin su.

Gwamnan na Zamfara ta cikin sanarwar dai, ya kuma ce, rayuwa da dukiyar al’ummar arewa na fuskantar barazana daga al’ummomin kudanci, wadanda ke cin zarafinsu a ko da yaushe.

Bello Muhammed Matawalle ya kuma ce wannan ba lokaci bane da za ayi amfani da siyasa, amma lokaci ne da ya zama wajibi mu gayawa kanmu gaskiya domin halin da ake ciki abin damuwa ne.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!