Labarai
Atiku ya bayyana jin daɗinsa kan hukuncin da Kotun Koli

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Alhaji Atiku Abubakar, ya bayyana jin daɗinsa kan hukuncin da Kotun Kolin kasar nan ta yanke dangane da rikicin shugabancin Jam’iyyar ADC.
Atiku ya bayyana hukuncin a matsayin wata nasara ga dimokuraɗiyya da kuma al’ummar Najeriya baki ɗaya, yana mai cewa wannan mataki ya nuna cewa tsarin shari’a na ƙasar nan na aiki yadda ya kamata.
Sai dai duk da haka, ya jaddada cewa har yanzu tafiyar ba ta ƙare ba, domin a cewarsa, akwai sauran aiki mai yawa wajen tabbatar da adalci da haɗin kai a cikin jam’iyyar.
Tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya kuma buƙaci mambobin jam’iyyar da magoya bayanta da su ci gaba da jajircewa da gwagwarmaya domin ganin an samu cikakken daidaito da ci gaba a harkokin siyasa.
You must be logged in to post a comment Login